DUNIYA MAKARANTA
:
Hattara da hawaye guda uku:
1. Hawayen iyaye
2. Hawayen maraya
3. Hawayen wanda ka zalunta.
:
DUNIYA MAKARANTA
Abu uku ba su amfani idan aka rasa abu uku:
1. Rayuwa idan babu lafiya
2. Kudi idan ba'a kyauta
3. Magana idan ba aiki.
:
DUNIYA MAKARANTA
Abu uku sanin su zai amfane ka:
1. Duniya ba a tabbata a cikin ta
2. Duniya babu hutu a cikin ta
3. Ba'a tsere wa zargin mutane
:
DUNIYA MAKARANTA
Abu uku suna batar da wasu uku:
1. Kudi suna boye aibi
2. Gori yana rufe dadin kyauta
3. Tsoron ALLAH yana boye son zuciya
:
DUNIYA MAKARANTA
Abu uku suna karfafa wasu uku:
1. Lafiya idan ta hadu da arziki
2. Bacci idan ya hadu da koshi
3. Dare idan ya hadu da ambaton ALLAH
:
:
:
:
DR. MANSUR Wrote.
Wata rana Sahabban manzon ALLAH (S.W.A)
sun kawo karar SAYYIDINA
ABUBAKAR gurin Manzon Allah (S.A.W)
suna Cewa Ya Manzon Allah: Abubakar ya
kasance idan muka hadu dashi yana riga
bamu hannunsa muyi musabiha cikin farin
ciki da sakin fuska, Amma yanzu idan muka
hadu dashi sai ya sunkuyar da kansa kasa
sai mun fara bashi hannun mu sannan zai
miko nasa. Sai manzon Allah yace aje maza a
kira Abubakar cikin lokaci sai gashi yazo
yana zuwa sai (S.A.W) yace kaji abin da
sahabbaina su ka fada gaskiya ne? Sai
Sayyidina Abubakar cikin girmamawa ya ce
ya wanda bakinsa baya karya, Eh hakane
gaskiya ne suka fada, Amma ina da hujja sai
yace jiya nayi mafarkin wani katafaren gida
wanda babu abinda ke cikinsa sai kayan
alfarma da more rayuwa da jin dadi wani
abin ma hankali da tunani baya misalta
su,Allah (S.W.A) ya fadamin cewa" babu
wanda zai shiga gidan face Wanda idan ya hadu
da mutane yana riga mika musu
hannu domin a gaisa kuma cikin sakin fuska
da murmushi", to shine nake musu
kwadayin
wannan gida da su shigeshi shi yasa na bari
su rinka fara miko min hannunsu suna farin ciki
da sakin fuska da murmushi.
Allahu Akbar !!! Don Allah dan uwa Kada Ka
Karanta ka barshi kai ka dai ka turawa 'yan
uwanka Musulmai Masoya Manzon Allah
(S.A.W) ?
jama'a don girman Allah Ku bada minti 2 domin
karanta
wannan babban sako, Manzon Allah saw yana
cewa : Ku
yawaita yin salati a gareni domin salatinku a
gareni to
haskene a gareku ranar tashin Alqiyama, ya Kara
da cewa
mutanen dake zaune a fadata ranar tashin
Alqiyama sune
masu yawan yimun salati, ya Allah muna rokonka
da
sunayenka 99 tsarkaka, ya Allah dan Sittin na
Alqurani,
ya Allah dan darajar Gadon Al-Arshi duk Wanda
ya tura
wannan sakon ga yan uwa musulmi Allah kaji
kansa, ka
gafartamasa kurakuransa, ka daukakashi akan
makiyansa
ya Allah duk bukatunsa na alkhairi ka biyamasa
ya Allah
ka tayar dashi a fadar manxon Allah saw ranar
tashin
Alqiyama, daga karshe ka sakashi Aljanna
madaukakiy,
Ameen, Allahumma Salli wa sallim ala
Nabiyurrahmati
Saw..